Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar tattalin arziki : Yemi Osinbajo ya nemi jihohi su kafa kwamitin tsaro

Published

on

Majalisar kula da tattalin arzikin kasa ta bukaci gwamnonin johohin kasar nan talatin da shida da su gaggauta kafa wani kwamiti na musamman kan harkokin tsaro da kuma kare hakkin bil adama, wanda zai rika sanya idanu kan ayyukan sabon sashen ‘yan sanda na musamnan da rundunar ‘yan sandan kasar nan ta kafa.

A daren jiya ne dai kwamitin ya fitar da sanarwar da ke ba da umarnin kafa kwamitin don kawo karshen cin zarafin jama’a da ake zargin ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro nayi.

Kwamitin kula da tattalin arzikin wanda mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ke jagoranta, ya kuma bukaci jihohin da su kafa wani kwamiti na musamman wanda zai rika karbar korafin jama’a wadanda suke zargin ‘yan sanda sun taba cin zarafinsu ko kashe musu ‘yan uwa .

Kwamitin na gwamnatin tarayya ya kuma bukaci al’ummar kasar nan wadanda suke zargin ‘yan sanda sun taba cin zarafinsu ko kashe musu ‘yan uwar ba bisa ka’ida ba, dasu zo gaban kwamitin na jihohi don gabatar da korafinsu,

A cewar kwamitin matukar aka binciko aka gano gaskiyar zargin da mutanen su ka yi, ba ko shakka gwamnatin za ta dauki tsauraran matakai don hukunta wadanda aka kama da laifi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!