Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Majalisar koli kan tattalin arzikin ta kafa kwamiti don nemo mafita kan rikice-rikice

Published

on

Majalisar koli kan tattalin arzikin Najeriya ta kafa wani kwamitin mutum goma domin nemo mafita kan rikice-rikice da ake yawan samu tsakanin manoma da makiyaya a kasar nan.

Kwamitin wanda mataimakin shugaban kasa farfesa Yemi Osinbajo ke jagoranta yana kuma kunshe da gwamnoni tara.

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje, ya ce; sauran mambobin kwamitin sun hada da gwamnonin jihohin Zamfara da Kaduna da Adamawa da Benue da Taraba da Edo Da Filato da Ebonyi da kuma Oyo.

A cewar sa tuni kwamitin ya fara taron sa na farko jim kadan bayan sanar da sunayen mambobin sa.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya kuma ce kwamitin ya sha alwashin gudanar da aiki tukuru domin samar da mafita kan rikicin da ake samu.

Tun da fari da ya ke karin haske kan taron majalisar kolin gwamnan jihar Ebonyi Dave Umahi, ya ce; mambobin kwamitin ba ya ga batun makiyaya sun kuma tattauna kan batun samar da kudade da za a rika samar da magunguna ga masu fama da cutar kanjamau.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!