Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Lafiyar kwakwalwa shi ne jigon rayuwar ko wane bil’adama – Likita

Published

on

Lafiyar kwakwalwa ita ce jigon gudanar da rayuwar ko wane bil’adama, inda take shafar mu’amala da kuma zamantakewar rayuwa, ta hanyar shafar yanayin tunanin ‘dan adam da kuma yadda yake gudanar da rayuwarsa baki-daya.

Likitoci sun bayyana cewar lafiyar kwakwalwa tana da matukar muhimmaci ga yaro da babba, yayin da rashin kulawa da lafiyar ka iya janyo matsaloli daban-daban, da suka hadar da tsoro ko rashin nutsuwa ko kuma jirkita yanayin tunanin dan adam.

Dr Aminu Abdullahi Taura, babban likita ne a sashen kula da lafiyar kwakwalwa na asibitin koyarwa na Aminu Kano, ya yi bayanin yadda ake ganewa idan mutum ya samu karancin lafiyar kwakwalwa.

Dr Aminu Taura ya kara da cewa kamata ya yi a baiwa lafiyar kwakwalwa muhimmanci, saboda rashin bayyanar illolin rashin lafiyar a jiki kan janyo hadari ga dan adam.

Bincike ya nuna cewa ko wane bil’adama yana cikin hadrin kamuwa da tabuwar lafiyar kwakwalwa, kasancewar cutar ba ta la’akari da shekaru ko jinsi ko kabila.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!