Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar wakilai ta ja hankalin jami’o’in kan karin kudin makaranta

Published

on

Majalisar wakilan Nijeriya ta gargadi jami’o’in kasar nan da kada su fake da sabon tsarin bada rancen kudin karatu ga dalibai wajen karin kuɗaɗen makaranta.

Wannan ya biyo bayan kudirin da ɗan majalisa Terseer Ugbor na jam’yyar APC daga jihar Benue ya gabatar a zaman majalisar.

A cewar sa tsarin bada rancen kuɗin karatu kamar yadda yake a mafiya yawan ƙasashen duniya tsari ne mai kyau dake baiwa masu ƙaramin ƙarfi damar samun ilmi, wadda ke zama ƙashin bayan ci gaban al’umma da tattalin arzikin ƙasa.

Don haka ne ma ya buƙaci majalisar wakilan tarayyar da ta tabbatar da aiwatar da tsarin bisa ƙa’ida kamar yadda aka shirya.

Rahoton : Asma’u Muhammad Sani

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!