Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar wakilai ta nemi INEC ta dawo da rarar kudin zaben 2015

Published

on

Majalisar wakilai ta bukaci hukumar zabe ta kasa INEC da ta dawo da kudaden da aka ware mata don gudanar da babban zaben kasa da aka gudanar a shekarar dubu biyu da goma sha biyar, wanda ya kai naira biliyan saba’in da uku.

Kwamitin kula da asusun gwamnati na majalisar wakilai, ya ce, ofishin akanta janar na kasa a waccan lokaci, ya sakarwa hukumar ta INEC da kudade da suka kai naira biliyan saba’in da uku don gudanar da babban zaben kasa a shekarar ta 2015.

Sai dai ya ce wannan kudaden basa cikin naira biliyan arba’in da biyar wanda tun farko aka amincewa hukumar ta INEC ta kashe don gudanar da zabukan.

Shugaban kwamitin kula da asusun gwamnati na Majalisar ta wakilai Wole Oke tare da sauran mambobin kwamitin sun bukaci hukumar ta INEC da ta dawo da wadannan kudade.

Majalisar ta kuma zargi ofishin akanta janar na kasa a waccan lokacin da yin gaban kansa wajen fitar da kudaden ba bisa ka’ida ba.

A bangare guda majalisar wakilan ta kuma bukaci akanta janar na kasa da ya dawo da wasu kudade da suka kai naira biliyan goma sha shida da miliyan dari tara wanda wani bangare ne na naira biliyan talatin da shida da miliyan dari tara da aka amince hukumar ta INEC ta kashe a shekarar dubu biyu da goma sha biyar, amma sai ofishin na akanta janar ya sakarwa INEC din da naira biliyan goma kacal.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!