Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Majalisar wakilai ta tuhumi babbar jami’a mai kula da shirin Npower

Published

on

Majalisar wakilai ta tuhumi babbar jami’a mai kula da shirin gwamnatin tarayya na samar da aikin yi ga matasa NPOWER Hajiya Maryam Uwais kan rashin sanya dukkannin masu ruwa da tsaki cikin shirin.

 

Shugaban kwamitin yaki da fatara na majalisar Muhammed Ali Wudil ne yayi wannan korafi lokacin da Hajiya Maryam Uwais ta jagoranci jami’an shirin, domin kare kunshin kasafin kudin su gaban kwamitin na majalisar wakilai.

 

A cewar Muhammed Ali Wudil, mambobin majalisar suna wakiltar dukkan-nin al’ummar kasar nan ne a don haka ba daidai bane a ce za a gudanar da shirin batare da tuntubar su ba, yana mai cewar, da an yi haka matsalolin zabar wadanda za su ci gajiyar shirin da ake fuskanta a yanzu da ba a same su ba.

 

Ya ce a yanzu kididdigar da suka samu ya nuna cewa yawancin al’ummar wasu yankunan kasar nan ne suka fi amfana da shirin.

 

Da take mai da jawabi Hajiya Maryam Uwais ta ce sun koyawa ma’aikatan gwamnati da kuma jami’an kananan hukumomi domin samun nasarar shirin.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!