Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar wakilai taki amincewa da karin firashin man fetur

Published

on

Shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai Ndudi Elimelu ya ce baza su amince da karin farashin man fetir da aka samu a baya-bayan nan ba, wanda ya tashi daga naira dari da arba’in da takwas zuwa dari da Hamsin da daya a kowacce lita.

Hakan na cikin wata sanarwa ce da shugaban marasa rinjayen ya sanyawa hannu, wadda ke dauke da kin amincewar su sakamakon yadda karin zai haifar da tashin farshin kayayyakin masarufi.

Ndudi Elimelu wanda dan majalisar tarayya ne daga jihar Delta, ya ce tashin farashin man fetur din zai kara ta’azzara tattalin arzikin kasar nan.

Bayan da aka yi karin farashin fetur da wuta kayan gwari bai sauya ba – kungiya

Abun da ya sanya NUPENG dakatar da rarraba man fetur a Legas

Mr Ndudi Elumelu ya kara da cewa, sakamakon hakan ne bangaren marasa rinjaye na majalisar wakilai suka ki amincewa da karin farashin man fetir din saboda la’akari da yadda ‘yan Najeriya ke rayuwa mai tsada a wannan lokaci.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!