Connect with us

Labarai

Majalisar zartaswa ta amince da ware fiye da Tiriliyan 68 don samar da lantarki a jamio’i da asibitoci

Published

on

Majalisar zartaswa ta Najeriya, ta amince da ware sama da Naira Tiriliyan 68 domin ayyukan samar da wutar lantarki a jamio’i da asibitocin koyarwa a faɗin ƙasar.

 

Ministan makamashi Adebayo Adelabu, ne ya bayyana hakan a ƙarshen taron majalisar a jiya alhamis, wanda shugaban ƙasa Bola Tinubu ya jagoranta.

 

Adebayo, ya ce, za a yi amfani da kuɗin ne domin taimakawa wajen samar da wuta a jam’ioi da asibitocin koyarwa guda 8 a faɗinNajeriya.

 

Ciki har da Jam’iar jihar Legas, da Jam’iar Ahmadu Bello da ke Zaria, sai Jami’ar Obafemi Awolowo da ke Ile-ife.

 

Sai kuma Jam’iar Najeriya da ke Nsukka, da Jami’ar Ibadan, da kuma Jam’iar Calabar da sauransu.

 

Ya kuma ce ana sa ran kammala ayyukan samar da wutan nan da watannin 7 zuwa 9.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!