Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Manoma sun biya kaso 24 na bashin Anchor Borrowers da CBN ya ba su- IMF

Published

on

Asusun bada lamuni na duniya IMF yace manoma sun biya kashi 24 cikin 100 na bashin da suka karba karkashin shirin Anchor Borrowers na Babban Bankin Kasa CBN.

Wannan na kunshe ne a cikin sabon rahoton kasa da kasa game da harkokin kudi mai taken ‘Nigeria: Selected Issues’.

Rahoton dai ya nuna cewa kashi 76 cikin 100 na rancen ba a biya asusun na IMF ba.

Tun a ranar 17 ga watan Nuwambar 2015 ne, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da shirin na Anchor Borrowers domin kulla alaka tsakanin kamfanonin da ke sarrafa kayayyaki da kuma kananan manoma.

A cikin rahoton na IMF ya kuma ce bashi a fannin noma a Najeriya bai yi wani tasiri wajen habaka bangaren ba, sakamakon gaza bawa wadanda suka dace da akeyi yayin bayar da bashin.

Rahoton: Abdukadir Haladu Kiyawa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!