Connect with us

Kasuwanci

Manoman Albasa sun tafka asarar Miliyoyin Naira sakamakon Iri maras inganci

Published

on

Manoman Albasa a jihar Kano na ci gaba da koka wa bisa yadda suka tafka asarar Miliyoyin Naira bayan da aka sayar musu iri maras inganci da ya janyo musu wannan asara.

A zantawar wakilinmu Auwal Hassan Fagge, da wasu daga cikin manoman Albasar a Kano, sun bayyana cewa, an shigo da irin ne daga kasar waje inda suka saya tare da yin amfani da shi sakamakon yadda a bara irin Albasar ya yi tsada.

Haka kun sun kara da cewa, tsadar da Iri ya yi ne ya janyo wasu suka shigo da shi cikin kasar nan inda manoma suka saya tare da yafa shi a gonakinsu.

“ Ni kaina na tafka asara sosaisakamakon amfani da wannan iri, a ido za ka ga irin ba shi da maraba da wanda muka saba amfani da shi, sai dai bayan da lokacin girbi ya yi sannan muka gano cewa maras kyau ne”, inji wani manomi Alhaji Lawan Sulaiman Gurjiya.

Haka kuma ya kara da cewa, “ Na san wani makwabcina wanda ya kashe fiye da naira 500,000 a noman Albasa, amma wadda ya samu ko naira 10,000 ba ta kai ba, don haka muna kira ga gwamnati da duk masu ruwa da tsaki da su gudanar da bincike kan wadanda suka shigo da wannan iri tare da daukar mataki a kansu idan suna sane suka shigo da shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!