Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Masarautar Ƙaraye ta mayar da Dagacin Madobawa kan kujerarsa

Published

on

Masarautar Ƙaraye ta janye dakatarwar da ta yiwa Dagacin Madobawa a ƙaramar hukumar Ƙaraye Alhaji Shehu Musa.

An janye dakatarwar ne bayan da kwamitin da aka kafa domin gudanar da bincike kan duk wani zargi da ake yi wa Dagacin ya gabatar da rahoton sa.

Masarautar ta buƙaci Dagaci da ya ci gaba da gudanar da mulkin al’ummarsa cikin kwanciyar hankali da gaskiya da adalci tare da daina yin duk wani abu da zai iya bata sunan masarautar.

Masarautar ta kuma gargaɗe shi da ya ci gaba da biyayya ga Hakiminsa da sauran masu riƙe da sarauta domin samun shugabanci nagari.

Idan dai za a iya tunawa, a kwanakin baya ne majalisar masarautar Ƙaraye ta sanar da dakatar da Dagaci Ƙauyen Madobawa saboda rashin gudanar da aikinsa yadda ya kamata.

Hakan na cikin sanarwar da jami’in hulɗa da jama’a na masarautar Haruna Gunduwawa ya aikowa Freedom Rediyo.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!