Connect with us

Labarai

Masarautar Kano ta tuɓe Rawani Mai Unguwar Ƴan Doya

Published

on

‎Mai martaba San Kano Khalifa Muhammadu Sunusi ll, ya sauke Mai unguwar Ƴan Doya da ke yankin karamar hukumar birni Malam  Murtala Hussaini Ƴan Doya daga kan mukaminsa sa bisa samun sa da laifuka da dama, tare da laifuka guda biyu na kin amsa umarnin kiran sarki a lokuta daban-daban da kuma rashin zaman sa a cikin talakawansa.

‎Mai martaba sarkin  ta bakin babban Dan majalisar, matawallen Kano Alhaji  Alhaji Aliyu Ibrahim Ahmad, ya bada umarnin sauke Mai unguwar daga kan mukaminsa na Mai unguwa.

‎Masarautar Kano ta ce, ba zata laminci duk wani rashin gaskiya da cin amana daga kowanne mai rike da sarauta gargajiya ba.

Don haka masarautar ta hori sauran masu rike da masarautu dasu guje rashin gaskiya da neman abun hannun talakawansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!