Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mata a karamar hukumar Warawa sun karbi tagomashi

Published

on

Sama da mata dari biyu Gwamnatin tarayya ta baiwa jarin Naira dubu goma goma a karamar hukumar Warawa domin su dogara da kansu.

Guda na Hukumar Samar da ayyukanyi ta kasa National Directorate of Employment  NDE Alhaji  Sanusi Yakasai ne ya bayyana hakan yau lokacin bikin rabon jari ga mata ‘yan Asalin karamar hukumar Warawa  dari biyu.

A cewar sa tun daga lokacin da Shugaban kasa Buhari ya hau kan mulki yayi alkawarin cigaba da yaki da Talauci domin bunkasa tattalin arzikin al’ummar kasar nan.

 

Alhaji Sanusi Musa ya kuma yi kira ga matan da suka ci gajiyar samun rabon jarin da su rike jarin hannu biyu- biyu tare da cigaba da gudanar da sana’oin su cikin taka tsan-tsan domin bunkasa jarin na su.

Tasirin talla ga ‘ya’ya Mata

Kungiyar Save the children da Action against hunger sun kaddamar da Shirin tallafawa al’umma a jihohin Kano da Kaduna.

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Abdulkarim Tukuntawa ya ruwaito cewa cikin wadanda da suka  halarci taron akwai Dagacin Garin Dau Alhaji Musa Adamu Musa da Babban Limamin  garin Dau da sauran al’ummar Karamar hukumar ta Warawa.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!