Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mata sun yi zanga-zanga a kano Kan ce-ce kucen kotun Ɗaukaka Ƙara

Published

on

Yayin da ƙungiyoyin Mata ke tada murya kan cece-kucen Kotun Daukaka Kara Kimanin mata sama da dubu daya ne suka gudanar da zanga-zanga a titunan Kano domin nuna damuwarsu kan batun.

Matan dauke da alluna da kwalaye suna rera wakokin goyon bayan gwamnan jihar Abba Yusuf sun tunkari Shalkwatar Ƴan sandan jihar inda suka mika takarda dauke da korafe-korafensu kan sakamakon hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke

Wannan shi ne karo na farko a tarihin Kano da mata suka fito kan tituna suna neman a yi wa dimokradiyya adalci tare da kare wa’adin zaben gwamna na ranar 18 ga Maris

Daya daga cikin masu zanga-zangar lumana Hajiya Rabi Hotoro ta ce suna kan tituna domin nuna damuwarsu kan abin da ya faru a kotun ɗaukaka kara

“Mun fito ne a yau saboda mun yi imani da dimokuradiyya da ƴancin kai na bangaren shari’a, muna son yin kira ga masu ruwa da tsaki da su yi abin da ya kamata tare da barin ra’ayin jama’ar Kano ya tabbata

” Kano ta fada cikin tashin hankali na siyasa biyo bayan cece-kucen da aka samu daga shari’ar daukaka kara inda hukunci na magana da rubuce-rubuce ya banbanta

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!