Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Mataimakin shugaban kasa ya gargadi sabbabin mambobin hukumomin kasa kaucewa cin hanci

Published

on

Mataimakin shugaban kasa, Ferfesa Yemi Osinbajo ya gargadi sabbin mambobin hukumomin kasar kaucewa cin hanci da rashawa a yayin gudanar da ayyukan su

Osinbanjo ya bayyana hakan ne, a ta bakin Sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha, lokacin da yake kaddamar da mambobin zuwa hukumomin da za su aikin su.

Osinbajo ya kuma bukaci mambobin su mayar da hankalan su, don inganta tattalin arzikin kasar nan.

A nasa bangaren, wanda ya yi jawabi a madadin sauran mambobin hukumomin, shugaban cibiyar nazarin harkokin mulkin kasar nan, Mista Ignatius Longian, ce wa ya yi, za su duk mai yiyuwa don ganin sun aiwatar da abun zai daukaka kasar nan a fadin duniya.

Sauran hukumomin sun hada da, hukumar kula da iyakokin kasar nan  da kuma hukumar lura da al’ummar da ke zaune a iyaykokin kasar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!