Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Matsin rayuwa: Za mu fara bankaɗo masu ɓoye kaya – Barista Muhuyi

Published

on

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Kano, ta yi barazanar kamawa tare da gurfanar da duk wani ɗan kasuwa da aka samu da laifin ɓoye kaya a wannan lokaci.

Shugaban hukumar Barista Muhuyi Magaji Rimin-Gado ne ya bayyana hakan a zantawarsa da manema labarai ranar Alhamis a ofishinsa.

Ya ce, tuni shirin su ya yi nisa na fara bincike tare da kama duk waɗanda aka samu laifin ɓoye kaya, la’akari da matsanancin halin matsin rayuwa da al’umma ke ciki a yanzu.

“idan ba ku manta ba, a duk lokacin da Azumi ya gabato ana samun wannan matsala, amma wannan hukuma ta mu muna yin tsayin daka wajen kawo ƙarshen matsalar, to yanzu haka ba za mu bari ba” a cewar Muhuyi.

Barista Muhuyi Magaji Rimin-Gado ya tabbatar da cewa, hukumarsu za ta kawo ƙarshen matsalar nan ba da daɗewa ba, kasancewar haƙƙin gwamnati ne ta kula da haƙƙin al’ummarta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!