Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano:Hukumar cin hanci da rashawa ta jihar ta kwato fiye da naira biliyan 4

Published

on

Hukumar Kula da Laifukan Cin Hanci da Rashawa ta jihar Kano ta ce ta kwato fiye da naira biliyan 4 da wasu kadarori daga wajen wasu al’umma da suke yi wa tattalin aziki zagon kasa a jihar Kano a shekaru hudun da suka wuce.

Shugaban hukumar Barista Muhiyi Magaji Rimin Gado ne ya bayyana haka a yayin da yake zantawa da manema labarai a jiya .

Bari. Muhuyi Magaji Rimin Gado ya ce tun bayan da ya fara aiki a ofishin hukumar ta samu damar sauraron korafai-korafan daga wajen kimanin mutane dubu goma sha hudu, haka nan kuma sun sami wasu sauraron korafai-korafai daga wajen wasu unguwanni guda dubu hudu.

Idan za’a Iya tunawa dai gwamnan Kano Abdullahi umar Ganduje ya nada Muhiyi Magaji Rimin Gado a Yunin  shekara ta 2015 a matsayin shugaban hukumar cin hancin da rashawa ta jihar Kano.

Ayyukan hukumar dai sun hadar da binciken ofisoshin ‘yan siyasa da wasu manyan ma’aikatan gwamnati ba tare da jin tsoro ko fargaba ba kamar yadda Muhuyi Magajin ke bayyanawa.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!