Labarai
Mazauna Dakata da kewayenta sun yi tattakin lumana na neman daukin gwamnati Kano

Mazauna unguwar Dakata da kewayenta, sun gudanar da tattakin lumana na ankarar da gwamnatin jihar Kano, mahukunta kama daga ‘yan Majalisar Jiha da Tarayya dangane da yi ko gyaran Titin Kwanar Kotu ta Jigirya zuwa Dakata Police Station da Kwanar Layin Isma’ila Mai Biscuit.
Tattakin ya gudana a yammacin jiya Lahadi karkashin jagorancin kungiyiyon gwagwarmaya na matasan yankin da suka taka tun daga kwanar Kotu har zuwa Dakata Police station.
Ya yin tattakin matasan dauke da Kwalaye sun bayyana cewar hanyar ta dade tana ci musu Tuwo a kwarya sakamakon mummunar lalacewar da ta yi duk da muhimmancin ta na hada bangarorin unguwannin da dama da tayi tare da manyan ma’aikatu da masana’antu da ke bangaren.
Da ya ke jawabi a ya yin gangamin shugaban gamayyar matasan da suka gudanar da tattakin koken , Muhammad Auwal, ya ce sun shirya gangamin ne domin kira ga mahukunta.
Dumbin matasan yankin na Dakata, da suka fito daga yankin Sabuwar Dakata da Tsohuwar Dakata, sai Jigirya , da Kawaji da yankin Yankaba ne suka fito gangamin tare da gudanar da tattakin don isar da sakon su ga hukumomi.
You must be logged in to post a comment Login