Connect with us

Labarai

Kotu ta yanke wa fitacciyar ‘yar TikTok hukuncin ɗaurin shekara 1 a gidan Yari

Published

on

Kotu a birnin Accra na ƙasar Ghana ta yanke wa wata fitacciyar ‘yar TikTok mai suna Camilla Alhassan, hukuncin ɗaurin shekara guda a gidan yari tare da yin aikin wahala, bayan samun ta da laifin yaɗa labaran ƙarya da kuma cin mutuncin tsohon Shugaban kasar John Dramani Mahama, a shafukan sada zumunta.

 

Camilla Alhassan mai shekaru 43, ta wallafa wasu bidiyoyi a shafinta na TikTok tana iƙirarin cewa John Mahama ya yi tsafi da shanu guda 32 domin ya lashe babban zaɓen ƙasar na shekarar 2024.

 

Ta kuma ƙara da cewa tallafin audugar Mata da aka raba wa mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a yayin yakin neman zaben wancan lokaci na da alaƙa da wannan tsafi.

 

A lokacin shari’ar, Camilla ta amsa laifukan da ake tuhumarta da su na yaɗa labaran ƙarya da kuma kalaman kiyayya da za su iya tayar da tarzoma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!