Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun Sahale dokoki guda 40 a majalisa ta 9- Majalisar dokokin Kano

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano, ta ce, ta samu nasarar sahale dokoki guda arba’in tare da karɓar ƙudu Ƙudurori fiye da 200 daga mambobinta a tsawon shekaru huɗu.

Shugaban majalisar Engr. Hamisu Ibrahim Chidari, ne ya bayyana hakan a ganawarsa da manema labarai bayan zaman majalisar ta 9 a yau Litinin.

Engr Hamisu Ibrahim Chidari, ya ƙara da cewa, bayan haka kuma, majalisar ta samu ƙarin wasu nasarori da dama musamman waɗanda suka shafi ci gaban al’umma.

Ya ƙara da cewa, daga cikin dokokin da majalisar ta samu nasarar sahalewa akwai dokar kare hakkin kananan yara da dokar kafa hukumar gudanarwar majalisar sai dokar kashe kudaden majalisar da sauransu.

Shugaban majalisar, ya kuma yaba wa ma’aikatan zauren bisa irin gudummawar da suka bai wa ƴan majalisa har suka samu damar gudanar da ayyukansu cikin lumana da ƙaunar juna.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!