Labarai
Mun samar da ofishin jami’an tsaro na musamman don gudanar da bikin Sallah cikin Tsari- KAZOMA

Hukumar kule da gandun Daji ta jihar Kano KAZOMA ta ce, ta samar da Ofishin Jami’an tsaro na musamman domin sanya Idanu kan yadda za a gudanar da bukukuwan Sallah a gidan adana namun daji na Zoo a bana.
Shugaban hukumar Musayyib Kawu Ungogo, ne ya bayyana hakan a zantawar sa da Freedom Radio kan irin shirin da hukumar ta yi a bikin Sallar Bana.
Haka kuma, Musayyib Kawu Ungogo, ya kuma ce, hukumar ta haramta gudanar da duk wani nau’in girki a gidan Musamman a lokacin bikin na Sallah.
You must be logged in to post a comment Login