Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mun shirya kawo ci gaba a ƙungiyar mata ƴan jarida – Aisha Bura

Published

on

Sabuwar Zaɓaɓɓiyar shugabar ƙungiyar mata ƴan jarida ta ƙasa Hajiya Aisha Ibrahim Bura ta alkawarta yin tafiya da kowanne ɓangare domin samar da haɗin kai da ci gaban mambobin ƙungiyar.

Hajiya Aisha Bura ta bayyana hakan a ranar Lahadi, jim kadan bayan kammala rantsar da ita a matsayin wadda ta samu nasarar lashe zaben da aka gudanar a daren ranar Asabar.

Ta ce, akwai buƙatar mambobin ƙungiyar su bata haɗin kai don ganin ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta.

“Za mu mutunta kowa mi yi tafiya da kowa, mu kuma bada horo ga mambobinmu domin su samu ƙwarewa” a cewar Bura.

Hajiya Aisha Ibrahim Bura ta samu nasara da kuri’u 498 yayin da abokiyar takarar ta kuma shugabar kungiyar mai barin gado Hajiya Ladi Bala ta samu kuri’u 381.

Tun a ranar Asabar ne aka buɗe babban taron ƙungiyar NAWOJ karo na 11, kuma a daren ranar ne aka yi zaɓen sabbin shugabanni, wanda mambobin ƙungiyar daga jihohin ƙasar nan 36 da birnin tarayya Abuja suka samu halarta.

Kuma zaɓen ne ya baiwa Hajiya Aisha Ibrahim Bura nasara tare da sakatariyar ƙungiyar Wasika Kadan da sauran ƴan takara.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!