Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Musulmai na zanga-zangar ƙyamar Faransa a Kano

Published

on

Al’ummar musulmi na gudanar da zanga-zangar nuna ƙyamar Faransa a birnin Kano.
Masu zanga-zangar sun fara tattaki da misalin ƙarfe 12 na ranar Lahadi daga Unguwar Gwammaja a ƙaramar hukumar Dala.
Image Block
Jagoran masu zanga-zangar Kwamared Mukhtar Nalele ya ce, ya zama tilas su nuna fushi kan kalaman ɓatanci da shugaban Faransa ke yiwa musulunci.
Nalele ya kuma buƙaci al’ummar musulmi da su ƙaurace wa sayen kayan ƙasar Faransa domin yin tir da abin da ke faruwa.
Masu zanga-zangar a Kano na ɗauke da kwalaye waɗanda aka rubuta saƙonnin nuna ƙyama ga Faransa da shugabanta.
Image Block
Me shugaban Faransa ya yi?
Jawabin shugaba Macron na cewa zai yaƙi addinin musulunci, shi ne ya fusata al’ummar musulmin duniya.
Jawabin ya biyo bayan kisan wani malamin makaranta mai suna Samuel Paty wanda ya nuna wa ɗalibansa zanen da aka yi na ɓatanci ga Annabi Muhammad (s.a.w).
Ƙasashen musulmi da dama ne suka shiga yin Alla-wadai tare da suka kan kalaman na Faransa.
Image Block
Ƙaurace wa kayan Faransa ya fara tasiri
Faransa ta buƙaci kasashen Gabas ta tsakiya da ka da su amince da kiraye-kirayen ƙaurace wa sayen kayayyakinta.
Ma’aikatar harkokin wajen Faransa ce ta bayyana hakan, wanda ke nuna fargaba kan fara ƙaurace wa kayayyakin nata.
Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!