Labarai
Mutane da dama sun jikkata sakamakon fashewa da gobara a Qatar

Mutane da dama sun jikkata bayan wata fashewa da gobara suka afku a yankin masana’antu na Ras Laffan da ke ƙasar Qatar a daren ranar Lahadi.
Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta Qatar ta bayyana cewa fashewar ta samo asali ne daga wata matsalar fasaha da ta faru a cikin ɗaya daga cikin masana’antun yankin, lamarin da ya haddasa gobara.
A wata sanarwa da ta fitar daga baya, ma’aikatar ta tabbatar da cewa matsalar fasahar ta janyo raunuka ga wasu mutane, sai dai ba ta bayyana adadin waɗanda suka jikkata ko kuma tsananin raunukan da suka samu ba.
Kamfanin QatarEnergy ya ce fashewar ta faru ne yayin da ake ƙoƙarin dawo da ayyukan cibiyar samar da iskar gas ta Barzan da ke cikin Ras Laffan Industrial City, inda gobara ta tashi bayan fashewar.
Ras Laffan na ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin samar da iskar gas mai ruwa (LNG) a duniya. Wurin ya taɓa fuskantar munanan hare-hare a lokacin rikicin da ya ɓarke tsakanin Amurka da Isra’ila a gefe guda da Iran a gefe guda.
You must be logged in to post a comment Login