Connect with us

Labarai

NCDC ta tabbatar mutuwar mutane 214 sakamakon zazzabin Lassa

Published

on

Hukumar Kula da Yaduwar Cutuka ta kasa NCDC ta ce cutar zazzabin Lassa ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 214 daga farkon shekarar da muke ciki ta 2026 zuwa yanzu. 

 

Hukumar ta bayyana cewa adadin mace-macen ya karu zuwa kashi 25 cikin 100, idan aka kwatanta da kashi 18.9 cikin 100 da aka samu a shekarar 2025 data gabata.

 

A cewar NCDC, sabbin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar a makonni 23 an samesu ne a jihohin Ondo, Edo, Bauchi da Ebonyi. 

 

Rahoton ya nuna cewa cutar ta bazu zuwa jihohi 23 da kananan hukumomi 109 a fadin kasar nan.

 

Hukumar ta ce matasa masu shekaru tsakanin 21 zuwa 30 su ne suka fi kamuwa da cutar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!