Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Mutanen gari sun ƙone waɗanda ake zargi da garkuwa da mutane a Kano

Published

on

Mutanen ƙauyen Rimi a ƙaramar hukumar Sumaila sun ƙone wasu mutane biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne.

Wannan al’amari ya faru ne da misalin ƙarfe 10:30 na daren ranar Juma’a.

Shaidun gani da ido sun ce, waɗanda ake zargin su uku ne, inda ɗaya daga cikin su ya miƙa kansa ga ofishin ƴan sanda.

Jama’ar garin a fusace sun yi ƙoƙarin ganin su hallaka shi, lamarin da yayi sanadiyar lalata wani sashe na ofishin ƴan sandan garin.

Rahotanni sun ce, ƴan sanda sun miƙa shi ga babban ofishin ƴan sanda na ƙaramar hukumar Sumaila.

Ƙarin bayani zai zo nan gaba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!