Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Mutum na 2 mai dauke da Corona ya rasu a Jigawa

Published

on

Da yammacin ranar lahadin nanne hukumomi a jihar Jigawa suka tabbatar da mutuwar mutum na biyu mai dauke da cutar Coronavirus.

Mai rasuwar dai wata matace daga karamar hukumar Miga, da aka gano tana dauke da cutar a baya-bayan nan, lokacin da yan uwanta suka kawota asibitin Jahun wadda daga bisani aka turasu asibitin kwararru na Rashid Shokoni dake Dutse, a nan kuma aka gano tana dauke da cutar.

Wakilinmu Muhd Aminu Umar Shuwajo ya rawaito cewa, a farkon satin da ya gabata ne mutum na farko ya rasu sakamakon cutar ta Coronavirus, wadda shikuma yana daga cikin mutum biyu da aka samu dauke da cutar a karamar hukumar Dutse.

Mutane tara ne ke dauke da cutar a Jigawa biyu sun mutu, sauran bakwai kuma suna cikin hayyacinsu da kuma samun kulawar likitoci, a cibiyar killace masu dauke da cutar dake Dutse a cewar hukumomin lafiya a jihar Jigawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!