Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Na kadu matuka da ganin sunayen mutanen da ke daukar nauyin Boko Haram – BUHARI

Published

on

Fadar shugaban kasa ta ce gwamnatin tarayya ta gano masu daukar nauyin ‘yan ta’addar Boko haram da ‘yan bindiga da ke ta kashe-kashen jama’a, babu gaira babu dalili a sassa daban-daban na kasar nan.

 

A cewar fadar shugaban kasa bankado wadanda ke da hannu cikin lamarin ya yi matukar kadata.

 

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu ne ya bayyana haka a daren jiya talata.

 

Mai taimakawa shugaban kasa kan harkokin yada labaran ya bayyana hakan ne ya yin zantawa da gidan talabijin na Channels, ya na mai cewa, ba za a saurarawa kowa ba komai girman mutum ko da kuwa dan siyasa ne matukar aka gano da hannunsa cikin lamarin za ayi mishi hukunci daidai da laifin da ya aikata.

 

Ya ce bincike ya gano cewa cikin masu daukar nauyin ‘yan boko haram da ‘yan bindiga akwai masu sana’ar canjin kudaden ketare wadanda suke da alaka da wasu gungun masu aikata laifuka na kasa da kasa da ke kasashen waje.

 

Malam Garba Shehu ya kuma ce gaskiya ne zargin da ake yi cewa akwai alaka tsakanin ‘yan boko haram da ‘yan bindiga da ke aikata ta’asa a wasu yankuna na kasar nan saboda akwai kwararan hujjoji da ya tabbatar da hakan.

 

Mai taimakawa shugaban kasa kan harkokin yada labaran ya kuma ce sun samu hujjoji da ke nuna cewa ana turo da makudan kudade ga kungiyar boko haram daga kasar hadaddiyar daular larabawa.

 

‘‘Tuni jami’an tsaro sun kama mutane da dama wadanda ake zargin suna da hannu cikin badakalar kuma ana ci gaba da bincike da zaran komai ya kammala za a bayyana sunayen su ga al’ummar kasa’’ a cewar Malam Garba Shehu.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!