Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Najeriya za ta karbi tallafin dala milyan 143 daga asusun tallafawa lafiya – Global Fund

Published

on

Najeriya za ta karbi jimillar kudi kimanin dala miliyan 143 daga asusun duniya na tallafawa harkokin lafiya wato ‘Global Fund’ don ci gaba da yaki da cutar tarin fuka.

A cewar asusun zai bai wa Najeriya kudaden ne cikin wa’adin shekaru uku masu zuwa.

Babban jami’in da ke kula da cututtuka a asusun Eliud Wanerdwalo ne ya bayyana hakan, yayin taron yaki da cutar tarin fuka karo na 33 da aka gudanar ta kafar internet.

Taron dai ya samu halartar ministocin lafiya da sauran masu ruwa da tsaki daga wasu kasashen afirka guda goma sha daya.

Ya ce jimillar kudaden da asusun zai tallafawa kasashen baki daya cikin shekaru uku masu zuwa ya kai dala miliyan dari biyar, inda Najeriya ita kadai za ta samu dala miliyan dari da arba’in da uku.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!