Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

A tabbatar an kashe kudaden tallafin da ake samu ga harkokin lafiya – Buhari

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci ministan Lafiya da ya tabbatar da an amfana da gudummawar da asusun tallafawa kasashe zai bayar ga Najeriya na dala miliyan 890, cikin shekaru uku masu zuwa.

Shugaban Najeriyar ya ce asusun ya shirya bada tallafin ne ga Najeriya don ci gaba da yaki da cutar kanjamau, tarin fuka da Malaria.

Shugaban ya bayar da wannan umarnin ne a wajen bikin kaddamar da tallafin dala miliyan 890, na shekarar 2021 da 2023, wanda kuma zai taimaka wajen karfafa ayyukan kiwon lafiya a kasar nan.

Muhammadu Buhari ya kuma ce Najeriya kasa ce da ke yaki da cin hanci da rashawa a don haka a kwai bukatar a tabbatar da an yi aiki da kudaden yadda ya kamata, musamman wajen dakile sabbin cututtukan da ke barazana ga al’umma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!