Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Najeriya zata zarce China yawan jama’a a nan gaba – Bincike

Published

on

Wani sakamakon bincike da jami’ar Washington da ke kasar Amurka ta fitar ya nuna cewa nan da shekaru tamanin masu zuwa adadin al’ummar Najeriya zasu zarce na kasar China yawa.

Kasar China dai a yanzu ita ce kasa mafi yawan al’umma a duniya, wanda bayanai suka ce nan da shekaru hudu masu zuwa, adadin jama’ar kasar ka iya kaiwa sama da biliyan daya da miliyan dari hudu.

Sai dai binciken da masana a jami’ar ta Washington, ya nuna cewa, nan da shekarar dubu biyu da dari daya adadin al’ummar kasar ta China zai yi matukar raguwa zuwa miliyan dari bakwai da talatin da biyu, lamarin da zai sa kasar Indiya ta zama kasa mafi yawan jama’a a duniya.

Jagoran masu binciken a jami’ar ta Washington, farfesa Christopher Murray, ya ce, nan da shekaru tamanin masu zuwa al’ummar Najeriya za su kai miliyan dari bakwai da casa’in da daya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!