Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

NPC;Ta ce adadin al’ummar kasar nan ya kai miliyan dari da casa’in da takwas

Published

on

Hukumar kidaya ta kasa NPC ta ce a yanzu haka adadin al’ummar kasar nan ya kai miliyan dari da casa’in da takwas, inda adadin al’ummar da ke rayuwa a birini ke karuwa da 6.5.

Shugaban hukumar kidayar ta kasa Mista Eze duruiheima ne ya bayyana haka a can kasar Amurka lokacin da ya ke bayani yayin taron tattauna batun yan gudun hijira da tattauna batun adadin al’ummar duniya karo na karo na 51

A cewar sa har yanzu Najeriya ita ce ke kan gaba a nahiyar Afrika wajen adadin al’umma, inda take kuma a mataki na bakwai a duniya duba da cewar yanzu al’ummarta ta kai miliyan 198.

Ya kara da cewa a hasashen da akayi nan da shekarar 2050 kasar nan za ta zama kasa ta uku a fadin duniya da ta fi kowacce kasa al’umma.

Ya kuma ce cikin shekaru 50 da suka wuce adadin al’ummar da ke rayuwa a birni ke karuwa, inda kowacce shekara ke karuwa da kaso 6.5 ba tare da karuwar ababen more rayuwa ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!