Connect with us

Labaran Kano

Zamu maye gurbin ma’aikatan da suka yi ritaya na Asibitin Murtala- Ganduje

Published

on

Gwamnati jihar Kano tace nan da makwanni biyu zata maye gurbin ma’aikatan lafiya dake Asibitin Murtala Muhammad wadanda suka yi ritaya da kuma wadanda suka mutu domin cigaba da bunkasa harkokin Lafiya a fadin Jihar Kano.

Shugabar Ma’aikata ta jihar Kano Hajiya Binta Lawan Ahmad ce ta bayyana hakan lokacin data kai wata ziyarar bazata tare da tawagar ma’aikatan Hukumar kula da ayyukan gwamnati zuwa Asibitin kwararru na Murtala domin ganin yadda ayyuka ke gudana.

Hajiya Binta Lawan Ahmad ta kuma yabawa shugaban Asibitin Murtala Muhammad Dr, Usaini Muhammad bisa yadda ta iske yana duba marasa lafiya da sanyi safiya kuma ta samu Asibitin cikin yanayi mai tsafta.

Da yake jawabi lokacin ziyarar Shugaban Asibitin Murtala Muhammad Dr Usaini Muhammad ya yabawa tawagar shugabar ma’aikatan tare da mika bukatar neman maye gurbin Ma’aikatan Asibitin da sukayi ritaya domin samarda ingantacciyar lafiya a Kano.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!