Connect with us

Ƙetare

Niger: Malaman makaranta sun janye yajin aikin da suka tsunduma

Published

on

Malaman makaranta a Jamhuriyar Nijar, sun sanar da janye yajin aikin da suka tsunduma a farkon makon nan da muke ciki.

 

Janye yajin aikin dai ya biyo bayan kawo karshen takun saka da aka kwashe tsawon lokaci ana yi tsakanin gwamnatin milkin soji a jamhuriyar ta Nijar da malaman makarantar kan batun biyan bashin da suke bin gwamnatin.

 

A ranar laraba ne dai ɓangarorin biyu suka cimma matsaya, lamarin da ya sa malaman janye yajin aikin da suka tsunduma a farkon mako wanda ya kasance karo na 4 a jere.

 

An dai kwashe tsawon lokaci ana tattaunawa, inda gwamnatin ta amince zata biya muhimman buƙatun malaman, ciki har da ɗaukan ma’aikata na din-din-din, hakazalika ta amince da biyansu alawus alawus da suke bi ta hanyar basu filaye domin a cewar gwamnatin, bata da isassun kudin da zata iya biyan bashin ma’aikatan 

 

Sai dai kungiyoyin malam  sun ce a shirye suke su koma yajin aikin sai baba ta gani  idan har gwamnati ta saɓa alƙawuran da ta ɗauka.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!