Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

NNPC ta tallafawa Kano da kayan yakar Coronavirus

Published

on

Kamfanin man fetur na kasa NNPC da abokan hurdarsa sun baiwa jihar Kano tallafin kayan aiki domin yakar cutar Covid-19.

Kayayyakin da suka bayar sun hada da na’urorin shakar iska da kayan kariya na jami’an lafiya da sauran kayayyaki.

Gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ne ya karbi kayayyakin a fadar gwamnatin Kano, inda ya mika su ga shugaban kwamitin tattara tallafi da rage radadi ga al’umma kan annobar Covid-19 Farfesa Yahuza Bello.

Wakiliyarmu Zahra’u Nasir ta rawaito mana cewa karamin ministan man fetur na kasa Timipre Marlin Sylva tare da shugaban NNPC Mele Kyari ne suka jagoranci tawagar kawo tallafin.

Har ila yau, tawagar tayi alkawarin cewa za ta ginawa jihar Kano asibitin yaki da cutuka masu yaduwa.

A nasa bangaren gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje yayi godiya da irin gudummuwar da suka kawowa jihar Kano a lokacin da take tsananin bukatar taimako.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!