Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

NUC:zata fara nazartar manhajar jami’oin Najeriya don bunkasa koyo da koyarwa

Published

on

Hukumar kula da jam’io ta kasa (NUC) ta ce  ta fara nazartar manhajar jami’oin kasar nan da nufin bunkasa harkokin koyo da koyarwa.

 

A cewar hukumar sake fasalin manhajar zai bai wa dalibai da suka kammala karatu a jami’oin kasar nan kwarewar da za su rika gogayya da takwarorinsu na kasashen duniya.

 

Shugaban hukumar ta NUC Farfesa Abubakar Rasheed ne ya bayyana haka a wajen bikin yaye dalibai karo na bakwai a wata jami’a mai zaman kanta da ke Abuja.

 

Ya ce gwamnati ta damu matuka kan yadda kamfanoni da hukumomi ke korafi game da rashin kwarewar dalibai da suka kammala karatu a jami’oin kasar nan.

 

Farfesa Abubakar Rasheed wanda wani darakta a ofishin babban sakatare Mr Chris maiyaki ya wakilta, ya ce, kwamitin na karkashin jagorancin tsohon shugaban hukumar ta NUC ne Farfesa Peter Okebukola.

 

Ya kuma ce, kwamitin na aiki dare ba rana don ganin an samar da manhaja ta bai daya da za ta da ce da zamanin da ake ciki

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!