Connect with us

Labarai

Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya yi gargaɗi kan yiwuwar harin ta’addanci

Published

on

Ofishin jakadancin Amurka da ke kasar nan ya gargaɗi ‘yan kasarm  kan yiwuwar harin ta’addanci da ka iya shafar cibiyoyin ta da kuma makarantu masu alaka da ƙasar a fadin Najeriya.

 

A sanarwar da ofishin jakadancin da ke Abuja ya fitar, an buƙaci ‘yan Amurka su ƙara yin taka-tsantsan idan za su ziyarci ofisoshin diflomasiyyar Amurka ko kuma cibiyoyin da ke da alaka da kasar.

 

Sanarwar ta ambaci ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja da kuma ƙaramin ofishin jakadancinta da ke Legas, inda aka buƙaci ‘yan kasar su kasance cikin lura tare da ɗaukar ƙarin matakan tsaro idan za su je waɗannan wurare.

 

Haka kuma ta shawarci ƴan ƙasar da su guji cunkoson jama’a ko zanga-zanga, sannan su sake duba tsare-tsaren tsaron kansu tare da iyalansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!