Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

PDP Kwankwasiyya ta nemi Aminu Wali ya bayyana a gaban kwamitin ladabtarwa

Published

on

Jam’iyyar PDP a nan Kano ta gayyaci ɗaya daga cikin jagororinta Ambasada Aminu Wali domin ya bayyana a gaban kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar.

A wata sanarwa da shugabancin jam’iyyar na mazaɓar Hotoron Kudu ya fitar, ta ce, ana zargin ambasadan da yiwa jam’iyyar zagon ƙasa a don haka aka gayyace shi domin ya zo ya kare kan sa.

Da yake karin bayani a kai, Sakataren yaɗa labaran jam’iyyar na jihar Kano, Bashir Sanata ya ce, ɗaukar wannan mataki ya zama dole, la’akari da zarge-zargen da suke yiwa ambasada Walin.

Sanata ya ce, ana zargin Ambasada Aminu Wali da ƙin bai wa jam’iyyar gudunmawa a zaɓen 2019.

Na biyu kuma yana mu’amala da Gwamnatin jam’iyyar APC a Kano, ta yadda baya iya yin hamayya da ita.

Sai dai har kawo lokacin da muke haɗa wannan rahoto, tsagin Aminu Wali bai ce komai ba a kan lamarin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!