Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

PDP ta bukaci a sauke hafsodhin tsaron Najeriya bisa gazawar su

Published

on

Jam’iyyar PDP ta bukaci shugaban kasa Muhammadu Buhari da ya sallami manyan hafsoshin tsaron kasar nan sakamakon gazawar su wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

A cewar jam’iyyar dabara ta kare ga manyan hafsoshin tsaron a don haka babu dalilin da za su c gaba da kasancewa a wannan mukami.

Mai Magana da yawun jam’iyyar Kola Ologbondiyan ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai, a Abuja.

Mista Kola Ologbondiyan ya ce abin kunya ne a ce tsawon lokacin manyan hafsoshin tsaron sun gaza wajen fitar da matsaya da zai kawo karshen zubar da jinin al’ummar kasar nan.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!