Labarai
PDP ta zargi APC da daukar matakan da ka iya jefa dimokuraɗiyya cikin hatsari

Jam’iyyar adawa ta PDP ta bayyana damuwa tare da zargin wasu matakan da jami’yar APC ke ɗauka a baya-bayan nan inda ta ce hakan na iya jefa dimokuraɗiyya cikin haɗari.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Ini Ememobong ya fitar, PDP ta ce abubuwan da ke faruwa na nuna alamun shirye-shiryen murƙushe jam’iyyun adawa, a babban zaben mai zuwa na shekara 2027.
Sanarwar ta zargi jam’iyyar mai mulki ta APC da ƙoƙarin lashe zaɓe ta kowace hanya, ko da hakan zai kawo cikas ga tsarin dimokuraɗiyya da kuma zaman lafiya a kasar nan.
PDP ta kuma nuna damuwa kan yadda wasu manyan hukumomi na ƙasa, ciki har da Hukumar Zabe ta kasa INEC musamman yadda take tafiyar da wasu al’amura da suka shafi jam’iyyun siyasa.
Jam’iyyar ta ce sabuwar sanarwar INEC kan batun shugabancin jam’iyyar ADC ƙarƙashin jagorancin David Mark ta ƙara tayar da hankali a ƙasar.
You must be logged in to post a comment Login