Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Pillars ta kadu kan tarar da LMC ya yi mata – Jambul

Published

on

Hukumar gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta ce tayi mamakin tarar da kamfanin shirya gasar League ta kasa LMC ya cita sakamakon hargitsin da ya faru a wasan ta da ta buga da Akwa United a ranar Lahadi 13 ga watan Yuni.

Shugaban kungiyar Alhaji Surajo Shu’aibu Yahya Jambul ne ya bayyana hakan ne jim kadan bayan da ya karbi sakon tarar daga LMC.

“Mun yi matukar kaduwa a lokacin da muka fara jin rade-radin an ci tarar mu, kafin daga bisani a aiko mana da takaddar tarar, “ inji Jambul.

Ya kara da cewa, Pillars bata sayar da tikitin shiga filin wasan ga kowa ba, haka kuma bata san yadda aka yi wadanda suka tayar da hargitsin suka shiga cikin filin ba.

Jambul ya kuma ce, “Kasancewar mu masu bin doka da oda zamu cigaba da yin duk mai yiwuwa don ganin mun ciyar da gasar League da kuma wasan kwallon kafa gaba, amma dai ya kamata a rinka yin adalci a dukkan lamura.”

Ya kuma shawarci masu ruwa da tsaki kan harkokin wasannin da su yi nazari kan abinda ya faru a lokacin da kungiyar ta Pillars da kuma takwararta ta Akwa United ke buga wasan don samo daidaito game da kura-kuran da akan tafka.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!