Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Rabon kwana ke kawo tabarbarewar aure a arewacin Najeriya – Malami  

Published

on

Limamin masallacin Usman Bin Affan da ke Gadon Kaya a nan Kano ya bayyana matsalar rabon kwana ga ma’aurata da cewa shi ne babbar kalubalen da ma’aurata ke fuskanta a rayuwar zamantakewar su ta yau da kullum.

Sheikh Ali Yunus ne ya bayyana hakan ta cikin shirin Barka da Hantsi na nan tashar Freedom Radiyo da ya mayar da hankali kan zamantakewar aure.

Ya ce, a shari’ance dare ne kwana ba rana ba, kamar yadda aka fi gani a wasu gidajen aure wajen rabon kwana, yana mai cewa ya danganta da yadda ma’auratan suka amince da rabon kwana a tsakanin su.

Ya kara da cewa, wajibi ne mutum yayi adalci tsakanin iyalansa akan rabon kwana tare da sauke nauyin zamantakewar aure kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.

Shaeikh Ali Yunus ya ja hankalin ma’aurata musamman maza da su tabbatar sun daidaita tsakanin matayen su wajen yin adalci wanda hakan zai basu damar tashi a gobe kiyama da cikakken jiki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!