Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rashin aikin yi ya karu da kaso 27% a bana – NBS

Published

on

Hukumar kididdiga ta kasa NBS ta ce, adadin wadanda basu da aikin yi a kasar nan ya karu daga kaso 23 zuwa sama da kaso 27 na tsakiyar shekarar da muke ciki wanda adadin ya zarta na shekarar 2018.

Hakan ne cikin wata kididdigar da hukumar ta fitar a baya baya nan, na adadin wadanda basu da aikin yi a kasar nan.

NBS ta ce adadin ya karu daga kaso 20 na kaso dayan shekarar 2018 zuwa sama da kaso 28 a kaso biyun shekarar da muke ciki.

Kididdigar ta NBS na nuna cewa, a kaso biyun farko na wannan shekara rashin aikin yi a kasar nan tsakanin matasa dake tsakanin shekara 15 da 34 ya karu daga kaso 29 zuwa sama da kaso 34, yayin da wadanda suke tsakanin wadannan shekaru kuma suke da ayyukan yi ya karu daga kaso 25 zuwa sama da kaso 28 kwatankwacin kaso ukun shekarar 2018.

Hukumar ta NBS ta kara da cewa, wannan adadi shi ne mafi yawa da aka taba gani, idan aka kwatanta da sauran shekaru a kasar nan.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!