Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

‘Yan Najeriya mazauna ketare 684 ne suka kamu da corona a kasashen waje – BOSS

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce kimanin ‘yan kasar nan 684 ne suka kamu da cutar corona a kasashen waje, yayin da dubu 13, 844 basa dauke da cutar, cikin adadin ‘yan kasar nan da aka dawo da su guda dubu 14, 906 wadanda suka makale a kasashen ketare sakamakon annobar corona.

Shugaban kwamitin yaki da cutar na gwamnatin tarayya Boss Mustapha ne ya bayyana hakan, lokacin da yake bada rahoto ga kwamitin yaki da cutar a birnin tarayya Abuja.

Ya ce, kwamitin ya lura da yadda matasa a kasar nan suka bada gudunmawa wajen yaki da cutar, a don haka abin a yaba ne matuka.

Boss Mustapha ya kara da cewa, fargabar da ake na yaduwar annobar a tsakanin al’umma ya ragu, sakamakon gudunmawar da kungiyoyin matasa ke yi na fito da dabarun wayar da akan al’umma.

Ta cikin jawabin nasa, Boss Mustapha ya ce, a yanzu kasar nan ta dawo da ‘yan asali kasar mazauna ketare su dubu 14, 906 tun bayan bullar annobar corona, wanda ya kawo kaso 80 na matafyan matasa ne.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!