Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rashin lauya yasa an samu tsaiko kan shari’ar AA ZAURA-EFCC

Published

on

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa a Nigeriya EFCC, ta ce an samu tsaiko kan cigaba da shari’ar dan takarar Sanatan Kano ta tsakiya Abdulsalam Abdulkarim, da akafi Sani da AA Zaura, bayan da jami’an ta suka gurfanar da shi a gaban Kotu, sakamakon rashin Lauyan sa da zai kare shi a Kotu.

A cewar hukumar ta bakin mai magana da yawun ta a nan jihar Kano Idris Muhammad, ya ce ‘wannna shi ne karo na hudu da ake samun tsaiko akan shari’ar ta dan siyasar , wanda a baya bai halarci Kotun ba a kashin kansa’.

https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2023/01/TRACK-UP-EFCC-ZAURA-31-01-2023.mp3-TRACK-UP-EFCC-ZAURA-31-01-2023.mp3-19.mp3?_=1

Ya kuma ce ‘rashin halartar Kotun da lauyan AA Zauran baiyi ba a jiya Litinin, ya sa mai shari’a ya sa Muhammad Nasir Yunusa, ya daga shariar zuwa ranar 6 ga watan Fabrairu mai kamawa don cigaba da gudanar da shari’ar tare da Lauyan wanda ake zargi, don bashi kariya.

Ana dai zargin AA Zaura, da Damfarar wani Balarabe dan kasar Kuwait Dalar Amurka Miliyan Daya da Dubu Dari Uku.

Rahoton: Abubakar Tijjani Rabiu

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!