Labarai
Rashin wutar Lantarki na taka rawa wajen karuwar fadan daba- Yan K/Naisa

Mazauna unguwanni Kofar Na’isa da Lokon Makera a Kano, sun koka da cewa rashin wadatacciyar wutar Lantarki ya jefa su cikin damuwa sakamakon yadda ɓata gari ke tayar da rikicin daba musamman ma a yan kwanakin nan.
Haka kuma mazauna yankunan, sun bayyana damuwa kan yadda suka kasance cikin halin duhu na tsawon lokaci bayan lalacewar Taransifomar su.
Mutanen sun kuma bayyana cewa duk inda ya kamata su nemi tallafi kama daga wajen mahukunta da sauransu sun bi amma abun ya ci tura.
A zantawarsu da Freedom Radio wasu daga cikin matan yankunan, sun roki gwamantin Kano da shugaban ƙaramar hukumar Gwale da su kai musu ɗauki.
Malam Dauda Lokon Makera na daga cikin Dattijan unguwar ya ce, kamata ya yi ƴan majalisa su mayar da hankali kan ayyukan da ya kamata ba wai rigima kan an bayyana wanda ya fi aiki a cikin su ba.
Sai dai duk ƙoƙarin da Freedom Radio ta yi na jin ta bakin ƙaramar hukumar ta Gwale da yankunan ke karkashinta, abun ya ci tura, sai dai za mu ci gaba da bibiyar wannan matsala.
You must be logged in to post a comment Login