Labarai
Rundunar Civil Defence ta kama mutane 6 da ake zargi da lalata bututu mai

Rundunar tsaro ta Civil Defence ta kama mutane 6 da ake zargi da lalata bututu tare da satar man fetur a yankin Pagada da ke a Karamar Hukumar Gwagwalada ta Birnin Tarayyar Abuja.
Wannan na cikin sanarwar da Jami’ar Hulda da Jama’a ta Rundunar, DSC Monica Ojobi, ta fitar.
Ta ce jami’an rundunar sun kama wadanda ake zargin ne da misalin karfe 3:30 na dare a ranar Asabar 18 ga Yuli, bayan samun bayanan sirri kan ayyukan da ake zargin suna yi a kusa da bututun.
Sanarwar ta ce, an kama su ne yayin da suke dibar man fetur suna durawa jarkoki bayan sun huda bututun da injin huda karfe.
Rundunar ta kwato babura biyu, jarkoki hudu masu dauke da man fetur, shebur daya, bindigogi gida biyu da injin huda karfe daya da ake zargin an yi amfani da shi wajen lalata bututun.
NSCDC ta ce ana ci gaba da bincike domin gano sauran wadanda ake zargin suna da hannu a lamarin.
You must be logged in to post a comment Login