Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar sojan sama ta lalata maboyar kungiyar ISWAP

Published

on

Rundunar sojan saman kasar nan ta lalata maboyar kungiyar ISIS ta yammacin Afrika dake Arewacin  jihar Borno.

Babban daraktan yada labarai na rundunar Air Commodore Ibikunle Daramola ya sanar da hakan a cikin wata sanarwar da ya fitar da ya fitar a yau a babban birnin tarayya Abuja.

Haka zalika rundunar ta kasha wasu daga cikin ‘ya’yan kungiyar a yankin Arrinna Ciki dake Tafkin Chadi.

Rundunar Sojan sama na Atisaye a Kano

Rundunar sojan Najeriya ta harbe yan bindiga 78 a watan jiya

Rundunar sojan kasar nan ta bukaci rufe offishin kungiyar Amnesty international

Air Commodore Ibikunle Daramola ya kara da cewar, rundunar ta gudnar da kai harin ne ta sama karkashin rundunar Operation LAFIYA DOLE.

A cewar sa babban daraktan yada labarai rundunar sojan saman ta aiwatar da aikin ne a tsakanin daya zuwa biyu ga watan Numban nan da muke ciki bayan ta samu bayanan sirrin dake nuna cewar ‘yan ta’adda na amfani da sansanin ne wajen kai hare-hare ga jami’an soja.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!