Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Rundunar sojin Najeriya ta kashe mayakan Boko haram 14 a titin Pulka zuwa Gwoza

Published

on

Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa ta samu nasarar kashe mayakan Boko haram guda goma sha hudu wadanda suka sace wata motar bus dauke da fasinjoji akan titin Pulka zuwa Gwoza a baya-bayan nan.

Haka zalika sojojin sun kuma samu nasarar ceto mutanen da ‘yan boko haram din suka sace su ashirin da uku yayin wani samame da suka kai kan maboyar su.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun rundunar Burgediya Janar Texas Chukwu.

Sanarwar ta ce, rundunar bataliya ta 192 ta Operation lafiya dole ce tare da hadin gwiwar sojojin sakai na civilian JTF da suka kai samamen.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!