Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Rundunar sojin Najeriya ta kashe mayakan Boko-haram 23 yayin wata arangama

Published

on

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta kashe mayakan Boko-haram guda ashirin da uku yayin wani batakashi da suka yi a yankin tabkin Chadi.

Daraktan yada labarai na rundunar,burgediya Janar Texas Chukwu ne ya bayyana haka ta cikin wata sanarwa da ya fitar jiya a garin Maiduguri.

Sanarwar ta ce, rundunar ta kuma samu nasarar kwato makamai da dama daga hannun ‘yan ta’addar.

Haka zalika burgediya Janar Texas Chukwu ta cikin sanarwar dai, ya kuma ce; ba ya ga wadanda suka rasa rayukansu mayakan na Boko-haram da dama kuma sun tsere da munanan raunuka.

A cewar sanarwar dakarun bataliya ta 153 tare da goyon bayan sojojin Kamaru ne suka yi kofar rago ga mayakan na Boko-haram.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!